Ma’aikatan layin dogo na Abuja sun bijirewa umarnin gwamnatin tarayya na zirga-zirgar jiragen kasa kyauta na kakar Yuletide wato Kirsimeti, yayin da su ke ci gaba da siyar da tikitin kan farashi mai tsada ga fasinjoji.
Peoples Gazette ta rawaito cewa, ma’aikatan tashar jirgin kasa ta Idu sun bayyana cewa sun sayar da tikitin ga fasinjojin da ke cikin jirgin Abuja zuwa Kaduna a kan kudi Naira 12,000 a safiyar ranar Asabar, da kuma N8,000 a yammacin ranar Juma’a.
Jaridar Gazette ta gano cewa tikitin jirgin kasa na yau da kullum ya kai kusan N2,000.
“Da safiyar yau a ranar Kirsimeti, jami’an layin dogo na cin hanci da rashawa na ci gaba da siyar da tikitin jirgin kasa na FG a tashar jirgin kasa ta IDU da ke Abuja har N12,000 ga ‘yan Najeriya. Babu shakka, Ma’aikatar Sufuri da NRA ba sa yin abin da ya dace, domin dakile wannan ta’addanci,” inji Deji Adesogan, wani fitaccen mai sharhi kan harkokin siyasa a Twitter.
Mista Adesogan ya kuma lura cewa matafiya da su ka dogara da hanyoyin balaguron sun sayi tikitin.
Fidet Okhiria, MD na Hukumar Jiragen Kasa ta Najeriya (NRC) ya sanar da zirga-zirgar jiragen kasa kyauta a fadin kasar daga ranar Juma’a 24 ga watan Disamba zuwa 4 ga Janairu, 2022. Ya shawarci fasinjoji da su rinka samun tikiti daga wuraren da su ka dace ba tare da tsada ba.
Amma wani mai amfani da Twitter, @Bizzylyks, shi ma ya yi ikirarin cewa, fasinjoji sun biya Naira 8,000 na tikitin zuwa yammacin ranar Juma’a.
“Yaron kawata da wasu abokan aurensu sun je gwajin kwallon kafa a Abuja, sun biya kudin tikiti a yau, sun sha wahala kafin ma su samu tikitin karfe 06:00 na yamma. Har ma na sanar da su cewa kyauta ne a yau,” ya rubuta har zuwa karfe 08:50 na dare. ranar juma’a.