fidelitybank

Jirgin Kasa Kyauta: Mutane na kokwa a kan siyan tikiti yayin tafiye-tafiye

Date:

Ma’aikatan layin dogo na Abuja sun bijirewa umarnin gwamnatin tarayya na zirga-zirgar jiragen kasa kyauta na kakar Yuletide wato Kirsimeti, yayin da su ke ci gaba da siyar da tikitin kan farashi mai tsada ga fasinjoji.

Peoples Gazette ta rawaito cewa, ma’aikatan tashar jirgin kasa ta Idu sun bayyana cewa sun sayar da tikitin ga fasinjojin da ke cikin jirgin Abuja zuwa Kaduna a kan kudi Naira 12,000 a safiyar ranar Asabar, da kuma N8,000 a yammacin ranar Juma’a.

Jaridar Gazette ta gano cewa tikitin jirgin kasa na yau da kullum ya kai kusan N2,000.

“Da safiyar yau a ranar Kirsimeti, jami’an layin dogo na cin hanci da rashawa na ci gaba da siyar da tikitin jirgin kasa na FG a tashar jirgin kasa ta IDU da ke Abuja har N12,000 ga ‘yan Najeriya. Babu shakka, Ma’aikatar Sufuri da NRA ba sa yin abin da ya dace, domin dakile wannan ta’addanci,” inji Deji Adesogan, wani fitaccen mai sharhi kan harkokin siyasa a Twitter.

Mista Adesogan ya kuma lura cewa matafiya da su ka dogara da hanyoyin balaguron sun sayi tikitin.

Fidet Okhiria, MD na Hukumar Jiragen Kasa ta Najeriya (NRC) ya sanar da zirga-zirgar jiragen kasa kyauta a fadin kasar daga ranar Juma’a 24 ga watan Disamba zuwa 4 ga Janairu, 2022. Ya shawarci fasinjoji da su rinka samun tikiti daga wuraren da su ka dace ba tare da tsada ba.

Amma wani mai amfani da Twitter, @Bizzylyks, shi ma ya yi ikirarin cewa, fasinjoji sun biya Naira 8,000 na tikitin zuwa yammacin ranar Juma’a.

“Yaron kawata da wasu abokan aurensu sun je gwajin kwallon kafa a Abuja, sun biya kudin tikiti a yau, sun sha wahala kafin ma su samu tikitin karfe 06:00 na yamma. Har ma na sanar da su cewa kyauta ne a yau,” ya rubuta har zuwa karfe 08:50 na dare. ranar juma’a.

nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...

An gargadi Borno da Yobe da Jigawa su zama cikin shirin ambaliya

Akwai yiwuwar samun ambaliya a jihohin Borno, Jigawa da...
X whatsapp