fidelitybank

Jirgin Emirate zai dawo da zirga-zirga Najeriya

Date:

Kamfanin sufurin jiragen sama na Emirates ya bayyana cewa zai koma zirga-zirga tsakanin Dubai ta Legas a Najeriya, shekara biyu bayan dakatar da jigilarsa a ƙasar.

Cikin wata sanarwa da kamfanin mallakin ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ya fitar, ya ce zai fara jigilar fasinja tsakanin ƙasashen biyu sau ɗaya a kowace rana daga ranar 1 ga watan Oktoba.

“Jigila tsakanin Legas-Dubai ya kasance mafi shahara tsakanin kwastomominmu na Najeriya, don haka muna fatan dawo da wannan jigila domin kyautata wa kwastomominmu don inganta harkokin kasuwancinsu da tafiye-tafiyensu”, in ji mataimakin shugaban kamfanin Emirates Adnan Kazim.

A watan Satumban 2022, kamfanin ya dakatar da jigila zuwa Najeriya, sakamakon tangarɗa da ta shiga tsakanin kamfanin da gwamnatin ƙasar, kan mayar wa kamfanin kuɗinsa da ya kai kimanin dala miliyan 85.

Najeriya – wadda ta fi kowace ƙasa yawan al’umma a nahiyar Afirka – na fama da ƙarancin kuɗin waje, lamarin da ya tilasta wa ƙasar taƙaita kuɗaɗen wajen ƙasar da take bai wa masu zuba jari a ƙasar don kwashe ribarsu.

A watan Maris ne Babban Bankin Ƙasar, CBN ya ce ya warware duka basukan waje da ake bin ƙasar da ya kai dala biliyan bakwai.

naija news today legits

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp