Kamfanin dakon kaya na kasar Hadaddiyar Daular Larabawa Emirates, ya tabbatar da cewa a ranar Alhamis zai ci gaba da gudnar da zirga-zirgar fasinjoji tsakanin Dubai da Najeriya daga ranar 5 ga ga watan Disamba, 2021.
Kamfanin jirgin ya ce zai yi zirga-zirga a Najeriya tare da jiragen saman sa, tare da baiwa matafiya daga Najeriya damar shiga Dubai cikin sauki ko zuwa hutu da kuma kasuwanci.
Sabon matakin dai, kamar yadda aka bayyana, wani mataki ne na warware takaddamar da ta yi da Najeriya kan dakatar da zirga-zirgar jiragen sama.
A cikin wata sanarwa da kamfanin ya fitar, a duk lokacin barkewar cutar  Korona na sabunta fasinjoji tare da matakan kiwon lafiya da samar da tsaro na masana’antu a kowane lokaci na yin balaguro, domin samun ci gaba da sadar da al’umma saboda farfado da tattalin arziki.