Kamfanin jiragen sama na Emirates ya sanar da dakatar da zirga-zirgar jiragen sama zuwa Najeriya bisa dalilin rashin dawo da kudaden shigar da yake samu daga kasar.
Ya ce matakin ya fara aiki ne a ranar 29 ga watan Oktoba.
A cikin wata sanarwa da kamfanin ya fitar a ranar Alhamis din da ta gabata, kamfanin ya ce ba shi da wani zabi illa ya dakatar da zirga-zirgar jiragen da ke zuwa Najeriya domin rage hasarar da ake yi.
Idan dai za a iya tunawa dai matakin da kamfanin ya dauka ya biyo bayan gazawar da babban bankin Najeriya ya yi na warware matsalar kudaden jiragen sama kasa da watanni uku bayan da a baya ya dakatar da zirga-zirgar jiragensa zuwa kasar a watan Agusta saboda gaza dawo da dala miliyan 85 na kudaden shiga. .
Sanarwar ta kara da cewa, “ Masarautar ta ci gaba da neman mafita domin dawo da sauran kudaden da aka toshe a Najeriya. Mun samu kwarin gwiwa daga kokarin Babban Bankin Najeriya na duba bukatar mu, kuma muka yi la’akari da cewa za a gaggauta warware wannan muhimmin lamari tare da cire kudaden da suka rage mana.
“A cikin wannan yanayi na ban mamaki, Emirates ba ta da wani zaÉ“i illa ta dakatar da zirga-zirgar jiragen sama zuwa daga Najeriya daga ranar 29 ga Oktoba 2022 don magance Æ™arin asarar da ke ci gaba.”