Wani daga cikin ‘yanuwan Mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya rubuta takardar korafi zuwa ga hukumar NCAA ta tarayya.
Daily Trust ta ce, Isa Sanusi Bayero wanda aka fi sani da Isa Pilot ne ya aika wasika ga hukumar kula da jiragen sama ta kasa NCAA, a kan abin da ya kira cin mutunci da aka yi wa Sarkin Kano.
Isa Sanusi Bayero ya zargi kamfanin jirgin Air Peace da cin zarafin Sarki da mutanen kasar Kano.
Alhaji Isa Pilot ya koka a kan yadda jirgin saman ya bata masu lokaci daga Banjul zuwa Legas, inda suka bata sama da sa’a guda. Bayan haka, ‘danuwan Sarkin ya fadawa hukumar NCAA cewa, kamfanin jirgin saman sun yi sanadiyyar da Mai martaba ya rasa jirgin da ya tashi zuwa Kano.
Rahotanni na nuni da cewa, Sarki Aminu Ado Bayero da ‘yan tawagarsa sun iso tashar jirgin na Legas ne minti 30 bayan jirgin Kano ya tashi.