Wani ƙaramin jirgin ɗaukar marasa lafiya ya faɗa kan rukunin gidajen al’umma a Philadelphia na ƙasar Amurka, lamarin da ya sa gidaje da motoci suka kama da wuta.
Lamarin ya ji wa mutane da dama rauni duk da dai har yanzu ba a tantance ɓarnar da ta afku ba.
Wani bayani da kamfanin jirgin saman kai agajin lafiya na Jet Rescue Air Ambulance ya fitar, ya ce jirgin ya kai ɗauki ne a ranar Juma’a inda yake ɗauke da yaro maras lafiya da mai jinyarsa da kuma ma’aikata huɗu.
Gwamnan jihar Pensylvania, inda abin ya faru, Josh Shapiro ya ce “mun san tabbas za a samu asarar rai, wannan haɗari abin takaici ne.”
Masu aikin ceto sun garzaya wurin yayin da mutane da karikitan jirgin suka cika titunan yankin.
Shaidu sun bayyana halin ruɗani da aka shiga inda mutane suka samu raunuka sannan ginegine suka kama da wuta.