Wata mata ta mutu a wani hatsarin jirgin kasa da ya afku a kan hanyar dogo daga Gwagwa zuwa Idu a babban birnin tarayya Abuja ranar Litinin.
A cewar majiyoyin ‘yan sanda, jami’an ‘yan sanda sun gano wanda abin ya shafa a sume a hanyar jirgin kasa da ke bayan Kamfanin Zeberced, tare da munanan raunuka masu kama da wani hadarin jirgin kasa.
“Bayan samun rahoton, nan take aka aika jami’an mu zuwa wurin, inda suka tarar da matar da dakakkiyar kai da karyewar kafafu,” majiyar ta bayyana.
An garzaya da mamacin zuwa babban asibitin Kubwa, inda jami’an lafiya suka tabbatar da rasuwar ta.
Tuni dai aka ajiye gawarta a dakin ajiyar gawa na asibitin domin a tantance gawarwakin ta.
Hukumomin kasar na kokarin zakulo wadanda suka mutu da kuma gano danginta.