fidelitybank

Jiragen Najeriya mara sa matuƙa na daga da zuwa – Turkiyya

Date:

Jakadan Turkiyya a Najeriya Hidayet Bayraktar ya ce jiragen helikwafta da marasa matuƙi da ƙasarsa ke ƙerawa za su isa Najeriyar nan ba da jimawa ba da zimmar tallafa wa ƙasar wajen yaƙi da matsalar tsaro.

Kamfanin dillancin labarai na NAN ya ambato, Bayraktar na magana yayin bikin Ranar Tarayyar Turkiyya karo na 99 da aka gudanar a ofishin jakadancin ƙasar da ke Abuja ranar Asabar.

Ya bayyana yunƙurin a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar da ƙasashen suka ƙulla a 2021, yana mai cewa Turkiyya za ta faɗaɗa taimakon da take bai wa Najeriya wajen yaƙi da barazanar tsaro.

“Yarjejeniyar da ƙasashenmu suka saka wa hannu a shekarar da ta gabata abu ne na tarihi,” a cewarsa.

“Ina mai farin cikin sanar da ku cewa nau’i biyu daga cikin jiragen yaƙinmu irinsu na farko, maras matuƙi na Bayraktar (TB-2) da helikwafta (T-149) ATAK na gab da isowa Najeriya.

“Muna da ƙwarin gwiwa cewa sabbin kayan yaƙi na Turkiyya za su taimaka wa gwamnatin Najeriya wajen samar da zaman lafiya da kare dukiyar ‘yan ƙasa.”

breaking news in nigeria today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp