Shugaba Biden da shugaban ƙasa mai jiran gado Donald Trump na jagorantar ta’aziyya da alhinin rasuwar tsohon Shugaban Ƙasa Jimmy Carter.
Biden ya bayyana shi a matsayin “jajirtaccen shugaba” kuma “cikakken dattijo”.
“A yau, Amurka da duniya, a ganina, sun yi rashin fitaccen shugaba, cikakken dattijo, mai tausaya wa al’umma,” in ji Shugaba Biden. “Ni da Jill mun yi rashin abokin arziki.”
A nasa ɓangaren, Donald Trump ya ce ya kamata Amurkawa “su gode wa Mista Carter kan kalubalen da ya fuskanta a lokacin shugabancinsa a wani muhimmin lokaci a tarihin Amurka”.
Carter ya rasu yana da shekara 100 a duniya.