fidelitybank

Jikar Nelson Mandela ta mutu

Date:

Zoleka Mandela, jikar zababben shugaban kasar Afirka ta Kudu na farko ƙarƙashin dimokuradiyya, Nelson Mandela, ta rasu tana da shekaru 43 sakamakon kamuwa da cutar daji.

Iyalanta sun sanar da rasuwar ta a shafin Instagram, inda suka bayyana cewa ‘yan uwa da abokan arziƙi da dama sun kewaye gawar tata.

A cikin ‘yan shekarun nan ta shahara wajen bayar da bayani game da cutar dajin da take fama da ita da kuma bayyana tarihinta na ɗabi’ar shan ƙwayoyi da tsananin damuwar da take shiga da kuma yadda aka yi lalata da ita tun tana ƙarama.

Zoleka ta kuma yi kamfe don samar da ingantaccen tsaro a kan titi bayan mutuwar diyarta mai shekaru 13 a wani hatsarin mota a shekarar 2010. Zoleka ta rubuta tarihin rayuwarta, wanda ta yi wa laƙabi da ‘when hope whispers’.

Ta kuma yi fama da cutar kansar nono sama da shekaru goma da suka wuce.

A shekarar da ta gabata ne ta tabbatar da cewa tana da cutar daji a hanta da huhu, daga nan kuma ta yadu zuwa wasu sassan jikinta.

nnnnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...
X whatsapp