Zoleka Mandela, jikar zababben shugaban kasar Afirka ta Kudu na farko ƙarƙashin dimokuradiyya, Nelson Mandela, ta rasu tana da shekaru 43 sakamakon kamuwa da cutar daji.
Iyalanta sun sanar da rasuwar ta a shafin Instagram, inda suka bayyana cewa ‘yan uwa da abokan arziƙi da dama sun kewaye gawar tata.
A cikin ‘yan shekarun nan ta shahara wajen bayar da bayani game da cutar dajin da take fama da ita da kuma bayyana tarihinta na ɗabi’ar shan ƙwayoyi da tsananin damuwar da take shiga da kuma yadda aka yi lalata da ita tun tana ƙarama.
Zoleka ta kuma yi kamfe don samar da ingantaccen tsaro a kan titi bayan mutuwar diyarta mai shekaru 13 a wani hatsarin mota a shekarar 2010. Zoleka ta rubuta tarihin rayuwarta, wanda ta yi wa laƙabi da ‘when hope whispers’.
Ta kuma yi fama da cutar kansar nono sama da shekaru goma da suka wuce.
A shekarar da ta gabata ne ta tabbatar da cewa tana da cutar daji a hanta da huhu, daga nan kuma ta yadu zuwa wasu sassan jikinta.