fidelitybank

Jihohin Arewa huɗu ne suke biyan mafi ƙarancin fansho na N32,000 – NUP

Date:

Ƙungiyar ƴan fansho na arewacin Najeriya, NUP ta ce jihohi huɗu cikin 19 na arewacin Najeriya ne kaɗai suke biyan mafi ƙarancin fanshon naira 32,000 da gwamnatin tarayya ta tsara.

Da yake bayani a taron shiyya na ƙungiyar a Kaduna, shugaban ƙungiyar, Kwamrade Mohammed Sali ya bayyana lamarin da “rashin adalci” da ya ce ake yi wa tsofaffin ma’aikatan bayan sadaukar da rayuwarsu da suka yi wajen aikin al’umma, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

“Jihohi huɗu ne kacal ke biyan mafi ƙarancin fansho na naira 32,000 a arewacin Najeriya mai jihohi 19. Akwai jihohin da suke biyan fanshon naira dubu 3,000 da 4,000 da 5,000,” in ji shi, inda ya ƙara da cewa ƙungiyar za ta fi mayar da hankali kan neman hanyoyin sasanci maimakon fito na fito da gwamnatocin jihohin.

“Ba za mu yi fito na fito da gwamnonin jihohin ba domin mu iyaye ne. Kuna so ku ga iyayenku a tituna suna gudanar da zanga-zanga? za mu zagaya jihohin mu tattauna da hukumomi domin samun sasanci cikin lumana,” in ji Sali.

sspdf news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp