fidelitybank

Jihohin Arewa huɗu ne suke biyan mafi ƙarancin fansho na N32,000 – NUP

Date:

Ƙungiyar ƴan fansho na arewacin Najeriya, NUP ta ce jihohi huɗu cikin 19 na arewacin Najeriya ne kaɗai suke biyan mafi ƙarancin fanshon naira 32,000 da gwamnatin tarayya ta tsara.

Da yake bayani a taron shiyya na ƙungiyar a Kaduna, shugaban ƙungiyar, Kwamrade Mohammed Sali ya bayyana lamarin da “rashin adalci” da ya ce ake yi wa tsofaffin ma’aikatan bayan sadaukar da rayuwarsu da suka yi wajen aikin al’umma, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

“Jihohi huɗu ne kacal ke biyan mafi ƙarancin fansho na naira 32,000 a arewacin Najeriya mai jihohi 19. Akwai jihohin da suke biyan fanshon naira dubu 3,000 da 4,000 da 5,000,” in ji shi, inda ya ƙara da cewa ƙungiyar za ta fi mayar da hankali kan neman hanyoyin sasanci maimakon fito na fito da gwamnatocin jihohin.

“Ba za mu yi fito na fito da gwamnonin jihohin ba domin mu iyaye ne. Kuna so ku ga iyayenku a tituna suna gudanar da zanga-zanga? za mu zagaya jihohin mu tattauna da hukumomi domin samun sasanci cikin lumana,” in ji Sali.

latest news in nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari a ƙauyuka 15 na Zamfara a mako ɗaya – Rahoto

Wani rahoto da tashar Channels ta ruwaito daga cibiyar Zamfara Circle...

Jihohin Arewa huɗu ne suke biyan mafi ƙarancin fansho na N32,000 – NUP

Ƙungiyar ƴan fansho na arewacin Najeriya, NUP ta ce...

A karon farko an gurfanar da Mutanen da ake zargi da kai hari Cocin Owo

Mutum biyar da ake zargi da shirya harin bam...

Peter Obi na nan a cikin jam’iyyar har yanzu – LP

Shugaban ƙungiyar Obidient Movement, Dr. Tanko Yunusa ya ce...

Yadda Mahara sun kashe mutum biyu, sun ƙona gidaje a Filato

Wasu da ake zargin mahara sun afka wa karamar...

An YI zanga-zanga a Isra’ila kan shirin Netanyahu na mamaye Gaza

Dubban mutane sun fito kan tituna a faɗin Isra'ila,...

Birtaniya za ta fara tisa ƙeyar bakin da suka aikata laifi zuwa kasarsu

Birtaniya ta fitar da sabon tsarin tisa keyar duk...

NDLEA ta kama Fasto kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Gwamnoni sun mika sakon ta’azziya ga iyalan Audu Ogbeh

Shugaban ƙungiyar gwamnonin arewa kuma gwamnan jihar Gombe, Muhammadu...

Duk wahala sai dai mu mutu a Gaza – Fatma

Wata mai mai ƴaƴa tara ta ce, duk runtsi...

Gwamnan Kano ya kori mataimansa na musamman kan belin Danwawu

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da...

Tsohon Minista a mulkin Buhari ya mutu

Allah ya yi wa tsohon ministan noma da raya...
X whatsapp