A wani rahoto da bankin na duniya ya wallafa tun ranar 1 ga watan Fabrairu kuma ya samu watsuwa a ranar 8 ga watan na Fabrairu ya fitar da bayan na sassan duniya da matsalolin yunwa da za su fuskanta.
A sashen Afirka ta yamma da ta tsakiya, rahoton mai taken ‘Food Security Update 2024’, ya bayyana cewa wasu jihohi guda bakwai na arewa maso yammaci da gabashi da wadanda za su fuskanci matsalar yunwa tun daga farkon shekarar nan har zuwa watan Mayu.
Jihohin dai su ne:
- Adamawa
- Borno
- Kaduna
- Katsina
- Sokoto
- Yobe
- Zamfara.
Rahoton dai ya bayyana dalilan rashin tsaro na ‘yan bindiga da ke satar jama’a a jihohi kamar Kaduna da Katsina da Sokoto da Zamfara, inda su kuma Borno da Yobe da Adamawa ke fuskantar matsalar Boko Haram.
Harwayau, rahoton ya yi wa jihohin kudin goro da sauran sassan Najeriya da ke fama da matsalar tsadar rayuwa a matsayin daya daga cikin dalilan da zai sa jihohin su fuskanci yunwa.
Da ma dai bankin na duniya a wani rahoto ya ayyana Najeriya a matsayin kasa ta 6 a jerin kasashen da suka fi talauci.