fidelitybank

Jihohin Arewa 7 a Najeriya za su fuskanci matsananciyar yunwa – Bankin Duniya

Date:

A wani rahoto da bankin na duniya ya wallafa tun ranar 1 ga watan Fabrairu kuma ya samu watsuwa a ranar 8 ga watan na Fabrairu ya fitar da bayan na sassan duniya da matsalolin yunwa da za su fuskanta.

A sashen Afirka ta yamma da ta tsakiya, rahoton mai taken ‘Food Security Update 2024’, ya bayyana cewa wasu jihohi guda bakwai na arewa maso yammaci da gabashi da wadanda za su fuskanci matsalar yunwa tun daga farkon shekarar nan har zuwa watan Mayu.

Jihohin dai su ne:

  • Adamawa
  • Borno
  • Kaduna
  • Katsina
  • Sokoto
  • Yobe
  • Zamfara.

Rahoton dai ya bayyana dalilan rashin tsaro na ‘yan bindiga da ke satar jama’a a jihohi kamar Kaduna da Katsina da Sokoto da Zamfara, inda su kuma Borno da Yobe da Adamawa ke fuskantar matsalar Boko Haram.

Harwayau, rahoton ya yi wa jihohin kudin goro da sauran sassan Najeriya da ke fama da matsalar tsadar rayuwa a matsayin daya daga cikin dalilan da zai sa jihohin su fuskanci yunwa.

Da ma dai bankin na duniya a wani rahoto ya ayyana Najeriya a matsayin kasa ta 6 a jerin kasashen da suka fi talauci.

sspdf news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp