Hukumar da ke yaƙi da cututtuka masu yaɗuwa ta Najeriya wato NCDC, ta bayyana cewa jihohi 23 ne ke fama da cutar sanƙarau a ƙasar.
Hukumar ta ƙara da cewa aƙalla mutum 315 ne suka kamu da cutar a jihohin Kebbi da Sokoto da Katsina, waɗanda kuma su ne sahun gaba a jerin jihohin da ke fama da wannan cuta.
Gwamnatocin jihohin dai sun bayyana ɗaukar matakan gaggawa domin daƙile yaɗuwar cutar a wasu matakai da suka ɗauka a jihohin nasu.