fidelitybank

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Date:

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana biyar ana ruwan sama kamar da bakin ƙwarya da ka iya janyo afkuwar ambaliyar ruwa a sassan jihohi 19 da kuma wasu wurare 76 a ƙasar.

Gargaɗin da aka fitar daga ma’aikatar muhalli ta ƙasar, ya buƙaci masu ruwa da tsaki da kuma mazauna yankunan da lamarin ka iya shafa da su ɗauki matakan kariya.

Hakan na zuwa ne yayin da mummunar ambaliya ta afku a jihohin Ogun da Gombe yayin da wasu jihohin da suka haɗa da Legas da Filato da Anambra da Delta suma matsalar ta shafe su.

A cewar sanarwar, ana hasashen yankunan za su samu mamakon ruwan sama a yankunan da zai iya haifar da ambaliya daga 5 zuwa 9 ga watan nan na Agusta.

Jihohin da hasashen ya shafa sun haɗa da Akwa Ibom da Bauchi da Ebonyi da Cross River da Nasarawa da Benue da Kaduna da Katsina.

Sauran jihohin sun haɗa da Kebbi da Kano da Neja da Filato da Taraba da Jigawa da Yobe da Zamfara da Sokoto da Borno da Gombe.

Matsalar ambaliya a Najeriya ta zama ruwan dare kowace shekara wadda ke janyo asarar rayuka da salwantar dukiya mai yawa.

A bara, jihohi 31 rahotanni suka bayyana sun yi fama da bala’in ambaliya da ta shafi mutum miliyan 1.2.

the sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp