Hukumar lafiya ta jihar Lagos ta soke sabbin dokokin zubar da ciki ta amintacciyar hanya, domin bayar da damar tuntubar bangarorin da suka dace.
An dai tsara dokokin ne shakara hudu da suka gabata domin bai wa kwararrun jami’an lafiya damar samar da hanyoyin zubar da ciki marasa hadari, to sai dai ba a tuntubi jagororin addini ba yayin tsara dokokin .
A farkon makon nan ne dai aka jiyo wani Fasto a jahar na cewa dokokin na kokarin halasta zubar da ciki ne kawai a fakaice.
A ranar Alhamis ne Gwamnan jihar Babajide Sanwo-Olu ya ce ana bukatar karin wayar da kan jama’a da masu ruwa da tsaki sosai domin kara fahimtar sabbin dokokin. In ji BBC.
Dokokin jihar Lagos dai sun bayar da dama da a zubar da ciki matukar aka fuskanci an mahaifiyar ko na dan tayin na cikin hadari, wadda kuma ake ganin ba lallai ne ya rayu ba.