fidelitybank

Jihar Kano ta APC CE – Akpabio

Date:

Shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, ya ce jihar Kano ta ci gaba da zama matattarar jam’iyyar All Progressives Congress, APC, gabanin zaben 2027.

Akpabio ya ce amincewar sa ta ta’allaka ne akan dabarun da mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau Jibrin, da shugaban jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje, da mai baiwa shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin majalisar dattawa, Sanata Basheer Lado ke da shi.

Shugaban Majalisar ya bayyana haka ne a wata ziyara da ya kai wa Lado a ofishinsa da ke majalisar dokokin kasar.

Ya kuma yaba masa bisa yadda ya tabbatar da sadarwa ta sirri tsakanin bangaren Zartarwa da Majalisar Dattawa, inda ya bayyana ayyukansa a matsayin wanda ba a taba ganin irinsa ba.

“Tare da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Shugaban Jam’iyyar APC na kasa, da kuma tasirin ku, Kano ta riga ta samu nasarar APC kafin 2027,” in ji Akpabio.

“Tun da Sanata Lado ya hau kan karagar mulki, ba a samu wata kwakkwarar bayanai ta sirri tsakanin fadar shugaban kasa da majalisar dattawa ba,” inji shi.

Akpabio ya nanata mahimmancin kiyaye sirri a cikin harkokin mulki, yana mai gargadin cewa zarge-zargen na iya yin illa ga tsaron kasa da yanke shawara.

Ya kuma amince da rawar da Lado ke takawa wajen inganta hadin gwiwa tsakanin bangaren Zartarwa da na Majalisa, da tabbatar da ingantaccen sadarwa da daidaitawa.

Ya kara da cewa, “Ayyukan da kuka yi a cikin watanni takwas da suka gabata sun yi fice, kun karfafa hadin gwiwa tsakanin bangaren zartarwa da na majalisar dokoki, inda ya kara da cewa.

nigeria legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp