Gwamnatin Jihar Edo, ta mayar da ranakun zuwa makaranta sau uku a sati da zimmar rage raɗaɗin cire tallafin man fetur da gwamnati ta yi.
Shugabar hukumar ilimin bai-ɗaya ta Edo State Universal Basic Education Board (SUBEB), Ozavize Salami ce ta bayyana hakan a Birnin Benin ranar Juma’a, kamar yadda kafar Channels TV ta ruwaito.
An ɗauki matakin ne bayan ganawar da ta yi da sauran hukumomin gwamnatin jihar domin fara aiki da umarnin gwamnati na rage yawan ranakun aiki daga biyar zuwa uku a makon da ya gabata.
“Game da matakin rage ranakun aiki zuwa uku a sati, mun yi ƙoƙarin mayar da ranakun zuwa makaranta cikin kwana ukun farko na kowane mako,” in ji ta.
Ta ƙara da cewa: “Ba ma son a samu wani tazgaro game da tsarin tafiyarwa. Saboda haka yara za su je makaranta a ranakun Litinin, da Talata, da kuma Laraba a dukkan makarantun firamare.
“Abin da muka yi shi ne, mun tsawaita lokacin koyarwa da awa ɗaya a firamare da kuma awa biyu a sakandare don tabbatar da cewa an cimma manhajar karatu da aka tsara.”