A ranar Alhamis din da ta gabata ne gwamnatin jihar Bayelsa ta nesanta kanta daga wani labarin da babban sakataren yada labaran gwamna Douye Diri, Daniel Alabrah ya wallafa a intanet, inda ya bayyana ra’ayinsa na kashin kansa na adawa da yunkurin da tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya yi na neman tsayawa takarar shugaban kasa a shekarar 2023 a karkashin jam’iyyar APC.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yada Labarai, Ayibaina Duba, ya fitar a Yenagoa.
Ya ce bayanin ya zama dole domin duk da cewa Alabrah ya bayyana karara cewa, ra’ayoyin da ya bayyana na kashin kansa ne, mutane da yawa sun yi kuskuren ra’ayinsa na kashin kan Diri da gwamnatinsa, saboda matsayin Alabrah na babban sakataren yada labarai ga gwamna.
Alabrah ya ce a cikin labarin da ya wallafa ta yanar gizo, “Ra’ayina shi ne”.