fidelitybank

Jigon jam’iyyar PDP ya marawa dan takarar gwamna APC baya a Oyo

Date:

Teslim Folarin, dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a jihar Oyo, ya samu amincewar Rashidi Ladoja, tsohon gwamnan jihar a karo na 1 a karkashin jam’iyyar PDP.

A kwanakin baya ne shugabanni da masu ruwa da tsaki na kungiyar goyon bayan tsohon gwamnan da aka fi sani da Ladoja Idera De suka bayyana goyon bayansu ga Sanatan da ke neman zama gwamnan jihar, inji rahoton Daily Trust.

Amma a ranar Asabar, 11 ga watan Maris, Ladoja ya fito fili ya amince da Folarin a wani taro da wasu magoya bayansa a Ibadan, babban birnin jihar Oyo.

Karanta Wannan: Na janye na baiwa shugaban majalisar dokokin Oyo – Adesope

Jigo a jam’iyyar PDP a jihar Oyo ya bayyana cewa, jam’iyya mai mulki a jihar ta sha kaye a hannun jam’iyyar APC a lokacin zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya da aka gudanar a jihar, saboda irin halayen gwamna Seyi Makinde.

Ya ce: “Kuma wannan ba ya shafi tarihin jihar Oyo, a’a har da tarihin wanda ke kan mulki. Mun ga misali da hakan a jihar Osun.” Ya kuma bayyana cewa, gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke, wanda ke kan karagar mulki a cikin watanni 3 kacal, ya samu nasarar wanke dukkanin ‘yan majalisar dattawa da na wakilai na jam’iyyar PDP a jihar.

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp