fidelitybank

Jigawa da Saudiyya za su bunkasa noman Dabino

Date:

Gwamnatin jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya za ta ƙulla hulɗar kasuwanci tsakaninta da wani kamfanin Saudiyya da ke noman dabino domin bunƙasa noman dabino a jihar.

Gwamnan jihar Umar Namadi ne ya bayyana haka a lokacin da ya karɓi baƙuncin ma’aikatan kamfani mafi girma a Saudiyya a fannin noman dabino da kula da aikin gona, karƙashin jagorancin Abdul’aziz Abdurrahman Al-Awf a Dutse, babban birnin jihar.

Abdul’aziz Al-Awf ya ce kamfaninsu za ta samar da tsarin noma na zamani domin ganin an yi noman dabino a tsawon shekara ba sai kaka ba, wanda za a cimma ta hanyar horar da manoma, karfafawa matasa da kuma amfani da wasu daga cikin ire-iren dabino na Saudiyya da ke samar da amfani mai yawa ta yadda jihar za ta zama kan gaba a noman dabino a Najeriya da Afrika.

Gwamnan jihar ya bayyana cikkakiyar goyon bayansa ga shirin, inda ya ce hakan ya yi dai-dai da manufarsa ta bunƙasa fannin noma.

Ya ce ko a yanzu ma jihar ce ta fi kowacce samar da dabino a Najeriya, kuma burinsu shi ne samar da adadin dabinon da ake buƙata a ƙasar har ma a fitar da shi ƙasashen waje.

Samfurin dabino na Mejdool (Meju) da Barhi (Bari) da Sukkari (Sukari) da kuma Ajwa ne aka bayyana a matsayin waɗanda suka dace a yi noman su a Jigawa.

www.nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...
X whatsapp