Wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP a masarautar Zuru ta jihar Kebbi, sun koma jam’iyyar APC mai mulki.
Kamfanin Dillancin Labarai na ƙasa ya ruwaito cewa, sarakunan da suka jagoranci masu sauya shekar sun hada da Alhaji Shehu Ribah daga Danko/Wasagu da Alhaji Nuhu Goma daga Zuru da Alhaji Adamu Jalalo daga Fakai da Alhaji Babuga Diri daga karamar hukumar Sakaba ta jihar.
Manyan jiga-jigan jam’iyyar APC ne suka tarbe wadanda suka sauya sheka a wani gangami da aka gudanar a jihar a ranar Lahadin da ta gabata, karkashin jagorancin mataimakin gwamna, Alhaji Samaila Yombe-Dabai da shugaban jam’iyyar, Alhaji Abubakar Kana-Zuru.
Yombe-Dabai, yayin karbar su cikin jam’iyya mai mulki, ya bayyana taron a matsayin “babban ci gaban siyasa” a jihar.
Ya kuma yi wa wadanda suka sauya sheka alkawarin shigar da su cikin dukkan al’amuran jam’iyyar APC a matsayin ‘ya’yan jam’iyyar na gaskiya.
“Muna yabawa Gwamna Atiku Bagudu bisa tabbatar da goyon bayan al’ummar jihar.
Mataimakin gwamnan ya ce “Wannan irin nasa ra’ayi ne ya sa jama’a su tafi jam’iyyar.”
Shugabannin wadanda suka sauya sheka sun dora laifin rikicin da ya barke a jam’iyyar PDP da barin jam’iyyar adawa.