fidelitybank

Jiga-jigan PDP sun sauya sheƙa zuwa APC

Date:

Wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP a masarautar Zuru ta jihar Kebbi, sun koma jam’iyyar APC mai mulki.

Kamfanin Dillancin Labarai na ƙasa ya ruwaito cewa, sarakunan da suka jagoranci masu sauya shekar sun hada da Alhaji Shehu Ribah daga Danko/Wasagu da Alhaji Nuhu Goma daga Zuru da Alhaji Adamu Jalalo daga Fakai da Alhaji Babuga Diri daga karamar hukumar Sakaba ta jihar.

Manyan jiga-jigan jam’iyyar APC ne suka tarbe wadanda suka sauya sheka a wani gangami da aka gudanar a jihar a ranar Lahadin da ta gabata, karkashin jagorancin mataimakin gwamna, Alhaji Samaila Yombe-Dabai da shugaban jam’iyyar, Alhaji Abubakar Kana-Zuru.

Yombe-Dabai, yayin karbar su cikin jam’iyya mai mulki, ya bayyana taron a matsayin “babban ci gaban siyasa” a jihar.

Ya kuma yi wa wadanda suka sauya sheka alkawarin shigar da su cikin dukkan al’amuran jam’iyyar APC a matsayin ‘ya’yan jam’iyyar na gaskiya.

“Muna yabawa Gwamna Atiku Bagudu bisa tabbatar da goyon bayan al’ummar jihar.

Mataimakin gwamnan ya ce “Wannan irin nasa ra’ayi ne ya sa jama’a su tafi jam’iyyar.”

Shugabannin wadanda suka sauya sheka sun dora laifin rikicin da ya barke a jam’iyyar PDP da barin jam’iyyar adawa.

nigerianewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp