Bayan sa’o’i 48 da gudanar da babban taron jam’iyyar (APC) na kasa wanda ta samar da Abdullahi Adamu a matsayin shugaban jam’iyyar na kasa, wasu jiga-jigan jam’iyyar adawa ta PDP sun yi taro don daidaitawa da samar da yankin Arewa, domin kai takarar shugaban kasa yankin kafin zaben fidda gwani na jam’iyyar.
Taron da aka gudanar a jihar Bauchi a ranar Lahadin da ta gabata ya samu halartar tsohon shugaban majalisar dattawa, Dakta Bukola Saraki, Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi, Gwamna Aminu Waziri Tambuwal na jihar Sakkwato, Kawu Baraje da kuma tsohon mataimakin gwamnan jihar Zamfara Mahdi Aliyu.
Idan dai za a iya tunawa, a shekarar 2021, jam’iyyar ta gudanar da babban taronta na kasa wanda ya samar da dan Arewa a matsayin shugabanta na kasa.
Sai dai da yake zantawa da manema labarai a karshen ganawar tasu, Saraki ya ce jam’iyyar PDP ce, kawai zabin da kasar nan ke da shi na ceto ta daga rugujewar da ke shirin yi, don haka akwai bukatar hadin kai da fahimtar juna, ya kara da cewa jam’iyyar iyali ce, da bai kamata ta hakura ba.