Tsoffin mataimakan gwamnoni biyu na jihar Kebbi, Ibrahim K. Aliyu da Mohammed Bello Dantani, Magajin Rafin Kabi tare da mataimakin shugaban jamâiyyar APC na shiyyar, Alhaji Atiku Alaramma Warrah da sakataren kungiyar na jiha, Abdullahi Mai Unguwa Shanga da wasu 43, sun sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar PDP.
A jihar Bauchi ma matan APC 5,000 ne suka sauya sheka zuwa PDP. A yayin da suke bayyana goyon bayansu a sakatariyar jamâiyyar PDP da ke Birnin Kebbi, babban birnin jihar a jiya, Aliyu da Kabi sun ce sun bar jamâiyyar APC ne saboda mugun hali da kuma gazawar gwamnatin jihar wajen aiwatar da ayyuka masu maâana a jihar.
Ya kara da cewa “Gwamnati ta yi alkawarin ba mu mukamai a lokacin zaben fidda gwanin da aka kammala na karshe amma ba a kammala komai ba,” in ji shi. Sun yi nuni da cewa babu yadda za a yi jamâiyyar APC ta samu nasara a zaben 2023 mai zuwa a jihar saboda âyaâyanta sun rasa kwarin gwiwa a jamâiyyar.
Shugaban jamâiyyar PDP, Alhaji Bello Suru, wanda ya samu wakilcin sakataren jihar, Alhaji Bawa Kalgo, ya yi maraba da su zuwa jamâiyyar tare da ba su tabbacin cewa za a yi musu daidai da lokacin da za ta kafa gwamnati a 2023.
Ya kuma ba su tabbacin cewa jamâiyyar za ta sauya salon shugabancinta idan ta hau mulki. An tarbi wadanda suka sauya sheka ne tare da masu ruwa da tsaki na PDP, Alhaji Abba Aliero, Alhaji Abubakar Atiku Bunu Jega, Alhaji Garba Maidoki Zuru, Alhaji Sani Dododo da dai sauransu.
A zantawarsa da LEADERSHIP, shugabar âyan takarar, Fatima Mohammed, ta ce sun kuduri aniyar komawa jamâiyyar PDP ne sakamakon gazawar gwamnatin tarayya karkashin jamâiyyar APC wajen cika alkawuran da ta dauka na fitar da âyan Najeriya daga kangin talauci da yunwa da dai sauransu.