Shugaban rukunin Dangote, Alhaji Aliko Dangote da Shugaban Kamfanin BUA, Alhaji Abdul Samad Rabiu, da wasu gungun ‘yan kasuwa za su hadu da Gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, a wajen kaddamar da tambarin tashar tsandauri ta Dala Dry Port, Kano.
Bude taron wanda zai gudana a Abuja ranar litinin, zai kuma hada da kaddamar da taron zuba jari na tattalin arzikin Kano.
Sanarwar da masu tallata tashar ta Dala ta fitar ta ce, “Batun kaddamar da taron shi ne share fage ga taron zuba jari na Kano wanda zai baje kolin tashar tsandaurin ta Dala a matsayin babbar hanyar sufuri da sauran fannoni kamar samar da tattalin arzikin Kano da zai bunkasa masana’antu da kasuwanci.
“Tashar tsandaurin ta mayar da Kano cibiya ta kasuwanci a cikin gida da waje, ta yadda za ta bunkasa tushen tattalin arzikin kasar.”
Sanarwar ta ce bude Logo da Jigon zai samu halartar manyan masu ruwa da tsaki a harkar da suka hada da; Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Ruwa ta Najeriya (NSC), Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa (NPA) Hukumar Kwastam ta Najeriya (NCS), Hukumar Kula da Tsaro da Kula da Jiragen Ruwa ta Najeriya, (NIMASA), Layukan sufurin Jiragen Ruwa, Hukumar Kula da Kayayyakin Kayayyaki (ICRC), da Babban Bankin Najeriya (CBN), Hukumar Kula da Jirgin kasa ta Najeriya (NRC), Hukumar Kula da Ruwa ta Kasa (NIWA) da Majalisar Dokokin Dakon kaya (CRFFN).”