Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya sanar da manyan Majalisar ta 10 a jam’iyyarsa ta APC a ɓangaren masu rinjaye.
Haka nan ya sanar da na marasa rinjaye, wato na jam’iyyun adawa.
Ga yankunan da na masu rinjaye suka fito:
- Sanata Opeyemi Bamidele – Shugaban Masu Rinjaye daga Jihar Ekiti (kudu maso yamma)
- Sanata David Umahi – Mataimakin Shugaban Masu Rinjaye daga Jihar Ebonyi (kudu maso gabas)
- Sanata Ali Ndume – Mai Tsawatarwa na Masu Rinjaye daga Jihar Borno (arewa maso yamma)
- Sanata Lola Ashiru – Mataimakin Mai Tsawatarwa na Masu Rinjaye daga Jihar Kwara (arewa ta tsakiya)
Yankunan da na marasa rinjaye suka fito:
- Sanata Simon Davou na PDP – Shugaban Marasa Rinjaye daga Jihar Filato (arewa ta tsakiya)
- Sanata Oyewunmi Olarere na PDP – Mataimakin Marasa Rinjaye daga Jihar Osun (kudu maso yamma)
- Sanata Darlington Nwokeocha na LP – Mai Tsawatarwa na Marasa Rinjaye daga Jihar Abiya (kudu maso gabas)
- Sanata Rufai Sani Hanga na NNPP – Mataimakin Mai Tsawatarwa na Marasa Rinjaye daga Jihar Kano (arewa maso yamma).