fidelitybank

Jarumin Nollywood da ya yi wa Tinubu addu’a tsigidir ya fadi dalilansa

Date:

Fitaccen jarumin fina-finan Nollywood kuma furodusa, Ebun Oloyede, wanda aka fi sani da Olaiya Igwe, ya bayyana dalilin da ya sa ya tafi tsirara a bakin teku domin yi wa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) addu’a, Bola Ahmed Tinubu ya samu nasara a zaben 2023.

Jarumin, a wani faifan bidiyo da aka watsa a shafin sa na Instagram ranar Asabar, an ga shi tsirara, yana addu’ar samun nasara ga Tinubu a bakin teku.

A cikin sakon nasa, Olaiya Igwe ya bayyana cewa tsohon gwamnan jihar Legas shine “dan takara daya tilo da ke nuna kimarmu da kyawawan manufofinmu. Kuma shugaban da zai yi fafutuka wajen ganin ya cika alkawarin da Najeriya ta yi wa al’umma masu zuwa.”

Instagram ya goge asusunsa saboda keta dokokinsa na tsiraici da batsa.

Ku tuna cewa a baya jarumin ya bayyana Tinubu a matsayin wanda ya taimaka masa domin ceto rayuwarsa bayan an gano shi da ciwon nephrolithiasis (Kidney Stones) ba tare da saninsa ba.

Mabiyan Olaiya a shafukan sada zumunta sun nuna rarrabuwar kawuna kan yanayin da ya zabi nuna goyon bayan sa. Yayin da mutane da yawa suka yi imanin cewa zai iya bayyana kansa ta kowace hanya da yake so, wasu suna ganin ya kamata ya yi amfani da wasu ladabi.

www.nigeriannewspapers.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp