fidelitybank

Jarumin Nollywood da ya yi wa Tinubu addu’a tsigidir ya fadi dalilansa

Date:

Fitaccen jarumin fina-finan Nollywood kuma furodusa, Ebun Oloyede, wanda aka fi sani da Olaiya Igwe, ya bayyana dalilin da ya sa ya tafi tsirara a bakin teku domin yi wa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) addu’a, Bola Ahmed Tinubu ya samu nasara a zaben 2023.

Jarumin, a wani faifan bidiyo da aka watsa a shafin sa na Instagram ranar Asabar, an ga shi tsirara, yana addu’ar samun nasara ga Tinubu a bakin teku.

A cikin sakon nasa, Olaiya Igwe ya bayyana cewa tsohon gwamnan jihar Legas shine “dan takara daya tilo da ke nuna kimarmu da kyawawan manufofinmu. Kuma shugaban da zai yi fafutuka wajen ganin ya cika alkawarin da Najeriya ta yi wa al’umma masu zuwa.”

Instagram ya goge asusunsa saboda keta dokokinsa na tsiraici da batsa.

Ku tuna cewa a baya jarumin ya bayyana Tinubu a matsayin wanda ya taimaka masa domin ceto rayuwarsa bayan an gano shi da ciwon nephrolithiasis (Kidney Stones) ba tare da saninsa ba.

Mabiyan Olaiya a shafukan sada zumunta sun nuna rarrabuwar kawuna kan yanayin da ya zabi nuna goyon bayan sa. Yayin da mutane da yawa suka yi imanin cewa zai iya bayyana kansa ta kowace hanya da yake so, wasu suna ganin ya kamata ya yi amfani da wasu ladabi.

vangurd 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gobara na cigaba da lakume wasu yankunan Turai

Gobarar daji na ci gaba da ruruwa a sassan...

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...

Gwamnati za ta gina titin jirgi a jihohi shida

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta haɗa gwiwa da...

Tinubu ya na cikin koshin lafiya – Farouk Adamu Aliyu

Tsohon ɗan majalisar wakilai daga jihar Jigawa, Faruk Adamu...

Amurka ta saka ladan dala miliyan biyar a kamo jagoran ‘yandaban Haiti

Amurka ta sanya dala miliyan biyar a matsayin lada...

Gwamnati ta janye karar da ta shigar kan Fasinjar jirgin Ibom

Gwamnatin Tarayya ta janye ƙarar da ta shigar kan...

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...
X whatsapp