Fitaccen jarumin fina-finan Nollywood kuma furodusa, Ebun Oloyede, wanda aka fi sani da Olaiya Igwe, ya bayyana dalilin da ya sa ya tafi tsirara a bakin teku domin yi wa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) addu’a, Bola Ahmed Tinubu ya samu nasara a zaben 2023.
Jarumin, a wani faifan bidiyo da aka watsa a shafin sa na Instagram ranar Asabar, an ga shi tsirara, yana addu’ar samun nasara ga Tinubu a bakin teku.
A cikin sakon nasa, Olaiya Igwe ya bayyana cewa tsohon gwamnan jihar Legas shine “dan takara daya tilo da ke nuna kimarmu da kyawawan manufofinmu. Kuma shugaban da zai yi fafutuka wajen ganin ya cika alkawarin da Najeriya ta yi wa al’umma masu zuwa.”
Instagram ya goge asusunsa saboda keta dokokinsa na tsiraici da batsa.
Ku tuna cewa a baya jarumin ya bayyana Tinubu a matsayin wanda ya taimaka masa domin ceto rayuwarsa bayan an gano shi da ciwon nephrolithiasis (Kidney Stones) ba tare da saninsa ba.
Mabiyan Olaiya a shafukan sada zumunta sun nuna rarrabuwar kawuna kan yanayin da ya zabi nuna goyon bayan sa. Yayin da mutane da yawa suka yi imanin cewa zai iya bayyana kansa ta kowace hanya da yake so, wasu suna ganin ya kamata ya yi amfani da wasu ladabi.