fidelitybank

Jarumin Indiya wanda ya yi fim ɗin Dus Numbari ya mutu

Date:

Fitaccen Jarumi da kuma mai shirya fina-finan Indiya, Manoj Kumar, ya mutu yana da shekara 87.

Jarumin ya mutu ne a birnin Mumbai bayan fama da jinya da ke da alaƙa da tsufa, a cewar DrSantosh Shetty na asibitin Kokilaben Dhirubhai Ambani, inda aka kwantar da shi.

Ɗan fitaccen jarumin, Kunal Goswami, ya faɗa wa kamfanin dillancin labarai na ANI cewa Kumar ya shafe tsawon lokaci yana fama da rashin lafiya.

Kumar dai ya bar gagarumin tarihi a masana’antar shirya-shirya fina-finai ta Indiya, inda ya haska a fina-finai da dama ciki har da Dus Numbari – waɗanda suka shi shahara a shekarun 1960 zuwa 1970.

Ƴan siyasa da taurari da kuma masoyansa na ta alhinin rasuwar tasa a shafukan sada zumunta.

Firaiminista Narendra Modi ya kira shi da “shahararren jarumi da ya haska sinimun Indiya”.

“Muna alfahari da ayyukan Manoj kuma za su ci gaba da ƙara wa masu tasowa ƙwarin gwiwa,” kamar yadda ya wallafa a shafinsa na X.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp