fidelitybank

Jarumar Kannywood ta gurfana a kotu da zargin bayar da na goro

Date:

An gurfanar da fitacciyar jarumar fina-finan Hausa Ta Kannywood A gaban kotun majistre da ke Gyaɗi-gyaɗi a Kano, bisa zargin yunƙurin bai wa ɗansanda cin hanci.

Ana zargin Amal da yunƙurin ba da cin hancin naira dubu 250 ga wani ɗan sanda mai suna ASP Salisu Bujama da ke rundunar ƴansandan, shiyya ta ɗaya da ke Kano.

A cewar mai gabatar da ƙarar, Amal na yunƙurin bayar da cin hancin ne domin hana binciken ƴan sanda kan zargin saurayinta da almundahanar kuɗi.

Lamarin ya bayyana ne lokacin da wani Yusuf Adamu ta hannun lauyansa ya shigar da ƙorafi ga mataimakin babban spetan ƴansanda Umar Mohammad Sanda, inda yake zargin saurayin jarumar da yin sama da faɗi da kuɗin da ya kai naira miliyan 40 da sunan kasuwanci.

Ƙorafin da aka shigar ya sa ƴansanda gudanar da bincike wanda ya gano cewa saurayin jarumar ya tura mata naira miliyan 13 ta asusun bankinta.

Acewar kakakin rundunar ƴansanda shiyya ta ɗaya, CSP Bashir Muhammed, an gayyaci ƴar fim ɗin domin amsa tambayoyi daga bisani kuma aka bayar da belinta sai dai an hana ta fita daga wata mota da ake zargin saurayin nata ne ya siya.

Jarumar ta tabbatar cewa kuɗin da ke cikin asusunta mallakin saurayinta ne duk da ta yi iƙirarin cewa naira miliyan takwas kawai ya tura mata.

Bayan da aka ba ta beli ne kuma ta garzaya babbar kotu a Kano domin neman a dakatar da ƴansanda daga binciken da suke a kanta. Kotun ta hana ci gaba da binciken da ƴansanda ke yi kan jarumar, abin da ya bai wa Amal dama ta yunƙurin ba da toshiyar baki ga ɗansandan da ke binciken ASP Salisu Bujama.

Jami’in ya yi watsi da cin hancin inda kuma ya kamata ta tare da shaidar zargin ba da cin hancin abin da ya sa aka gurfanar da ita gaban kotun majistre ranar Laraba.

Laifin da ake zargin jarumar ta aikata ya saɓa sashe na 118 na dokar penal code wadda ta haramta bai wa jami’in ɗansanda cin hanci.

bbc news nigeria today live

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp