Wani jariri dan watanni 19 ya fada cikin wata rijiya da ke unguwar Al-Ansar Quarters da ke karamar hukumar Danbatta a jihar Kano.
Kakakin hukumar kashe gobara ta jihar, SFS Saminu Abdullahi, ya ce, sun samu kiran gaggawa daga wani Salisu Bello inda suka aika da tawagar ceto zuwa wurin.
Hukumar ta ceto gawar yaron daga rijiyar yayin da hukumar ta fara gudanar da bincike kan lamarin, in ji shi.
Ya yi kira ga iyaye da su kasance masu lura da harkar ‘ya’yansu, domin gujewa irin wannan yanayi mara dadi.
Ya kuma umarci mazauna garin da su yi kokarin gina katanga masu tsayi a kusa da budadden rijiyoyinsu tare da yin amfani da karafa wajen rufe su. a cewar kamfanin dillancin labarai na kasa NAN.