Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin cewa rage kuɗaɗen tallafi na iya kawo cikas ga ci gaban da aka samu na rage mace-macen mata a wajen haihuwa.
Wani rahoto da hukumar lafiya ta duniya ta fitar ya ce mace-macen masu juna biyu da kuma wurin haihuwa ya ragu da kashi 40 cikin ɗari sai dai masana sun ce ci gaban ya ragu kuma ana fargabar adadin zai sake ƙaruwa saboda dakatar da tallafin da Amurka ke bayarwa.
A shekarar 2023 mata masu juna biyu ɗubu ɗari biyu da sittin aka bayar da rahoton sun mutu, wato kwatankwacin a ce mace ɗaya na mutuwa duk bayan minti biyu.
Kuma ƙasashen Afrika ne matsalar ta fi ƙamari a ƙasashen Chadi da Najeirya da Somalia