fidelitybank

Jamus za ta tallafawa da Afrika dala biliyan 4.4

Date:

Shugaban Gwamnatin Jamus Olaf Scholz, ya yi alƙawarin samar da dala biliyan 4.4 nan da 2030 ga shirin samar da makamashi maras gurɓata muhalli tsakanin Tarayyar Turai da ƙasashen Afirka.

Yayin ganawa da ƙasashen Afirka da na ƙungiyar G20 a birnin Berlin ranar Litinin, shugaban ya bayyana aniyar sayo “mafi yawan” makamashin da ƙasarsa ke buƙata daga Afirka.

Shirin zai taiamaka wajen samar da wutar lantarki, da dogaro da kai wajen makamashi, da kuma faɗaɗa kasuwanci a nahiyar Afirka.

An ƙirƙiri ganawar tsakanin ƙasashen Afirka da G20 ne a 2017 da zimmar haɓaka tattalin arzikin Afirka ta hanyar ƙara yawan jari.

Jami’an gwamnatin Jamus na ganin Afirka za ta taimaka wa ƙasarsu, wadda ta fi kowacce girman tattalin arziki a Turai, wajen faɗaɗa hanyoyin samun makamashi, da samun ƙwararrun ma’aikata, da rage yawan baƙin-haure, da kuma cimma muradun kyautata muhalli.

A shekarar da ta gabata, kasuwanci tsakanin Jamus da ƙasashen Afirka ya kai darajar dala biliyan 65.4, wanda wani kaso ne kawai na adadin kasuwancin da ƙasar ke yi da ƙasashen Asiya.

latest nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp