Shugaban Gwamnatin Jamus Olaf Scholz, ya yi alƙawarin samar da dala biliyan 4.4 nan da 2030 ga shirin samar da makamashi maras gurɓata muhalli tsakanin Tarayyar Turai da ƙasashen Afirka.
Yayin ganawa da ƙasashen Afirka da na ƙungiyar G20 a birnin Berlin ranar Litinin, shugaban ya bayyana aniyar sayo “mafi yawan” makamashin da ƙasarsa ke buƙata daga Afirka.
Shirin zai taiamaka wajen samar da wutar lantarki, da dogaro da kai wajen makamashi, da kuma faɗaɗa kasuwanci a nahiyar Afirka.
An ƙirƙiri ganawar tsakanin ƙasashen Afirka da G20 ne a 2017 da zimmar haɓaka tattalin arzikin Afirka ta hanyar ƙara yawan jari.
Jami’an gwamnatin Jamus na ganin Afirka za ta taimaka wa ƙasarsu, wadda ta fi kowacce girman tattalin arziki a Turai, wajen faɗaɗa hanyoyin samun makamashi, da samun ƙwararrun ma’aikata, da rage yawan baƙin-haure, da kuma cimma muradun kyautata muhalli.
A shekarar da ta gabata, kasuwanci tsakanin Jamus da ƙasashen Afirka ya kai darajar dala biliyan 65.4, wanda wani kaso ne kawai na adadin kasuwancin da ƙasar ke yi da ƙasashen Asiya.