fidelitybank

Jam’iyyun siyasa ku ajiye batun zaɓe mu tunkari matsalar tsaro – Buhari

Date:

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, ya yi kira ga dukkan jam’iyyun siyasa a kasar da su ajiye batutuwan zabe a gefe guda, kuma su hada hannu da gwamnatinsa a kokarin da take yi na magance matsalar tsaro.

Shugaban ya bayyana haka ne yayin da wasu jami’an jam’iyun suke shan ruwa a Fadar Aso Rock tare da wasu manyan ‘yan kasuwa, inda ya ce, rashin tsaro shi ne babbar matsalar da ke damun kowane dan Najeriya.

Shugaban ya ce a makon jiya, yayin taron babban kwamitin gudanarwa na jam’iyyarsa ta APC, an fitar da kwakkwarar matsaya cewa jam’iyyar za ta ci gaba da kokarin karfafa turakun dimokradiyya a dukkan matakan mulki na kasa.

Ya kuma tabo batun saukaka kasuwanci a kasar inda ya shaida wa manyan ‘yan kasuwan da ke dakin cewa, gwamnatinsa ta taka rawar gani a fagn inganta yanayin kasuwanci a Najeriya, sannan ya bukaci su taimaka ma ta wajen kawar da talauci da samar da ayyukan yi ga matasa:

“Babu gwamnatin da ta yi aiki mai yawan namu a bangaren samar da daidaitaccen yanayi da renon kasuwanci ga manya da kananan kamfanoni domin su bunkasa.

Yayin da yake magana a madadin jam’iyyun siyasa da suka halarci shan ruwan, Injiniya Yusuf Yabagi, wanda shi ne shugaban jam’iyyar Action Democratic Party (ADP) ya bayyana shugaba Buhari a matsayin mai yekini gina dimokradiyya na gaske.

‘Yan kasuwan da suka halarci shan ruwan ma sun yi tsokaci, inda Mista Kola Adesina wada shi ne shugaban kamfanin Sahara Group, ya ce tilas shugaban da zai gaji Muhammadu Buhari “ya rungumi salon karfafa gwuiwar jama’ar kan samar da sabuwar Najeriya, ba gina kansa ba kawai.

vanguard news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp