fidelitybank

Jam’iyyun adawa sun yi watsi da tattaunar shugaban kasar Senegal

Date:

Jam’iyyun adawa a Senegal sun yi fatali da shiga tattaunawar da shugaban ƙasar Macky Sall ya gabatar ta yin taron tsayar da sabuwar ranar zaɓen shugaban ƙasar bayan da ya sanar da ɗage zaɓen a farkon wannan wata.

Da alama dai rikicin siyasar ƙasar Senegal bai kare ba bayan da ƴan takarar shugaban kasa 16 daga cikin 19 na adawa suka ce ba za su shiga tattaunawar ba, wadda aka shirya gudanarwa a farkon mako mai zuwa.

Kungiyoyin farar hula da dama su ma sun yi fatali da batun tattaunawar.

Wannan ya biyo bayan jawabin da shugaba Macky Sall ya yi ta talabijin a daren ranar Alhamis, inda ya yi alƙawarin yin murabus a ƙarshen wa’adinsa, ranar 2 ga Afrilun 2024, sai dai bai bayyana sabuwar ranar da za a gudanar da zaɓen ba.

Mista Sall, wanda ke kan hanyarsa ta zuwa Abuja domin halartar wani babban taro na kungiyar ECOWAS, na fuskantar matsin lamba kan ya sanya sabuwar ranar zaɓe, tun bayan da majalisar ƙoli ta shari’a ta ƙasar ta bayyana ɗage zaɓen a matsayin haramtacce.

Yunƙurin ɗage zaɓen ya samu kakkausar suka daga ƙasashen duniya, waɗanda ke kallon Senegal a matsayin ɗaya daga cikin ƙasashe masu tafiyar da mulkin dimokuradiyya kan tsari mai kyau, yankin da ake fama da juyin mulkin a yankin Yammacin Afirka.

national tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp