fidelitybank

Jam’iyyun adawa sun maka Tinubu a kotu

Date:

Jam’iyyun adawa hudu a Najeriya sun shigar da ƙara domin ƙalubalantar nasarar zaɓaɓɓen shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar ranar 25 ga watan Fabrairun da ya gabata.

Dan Takarar jam’iyyar PDP Atiku Abubkar da na LP Peter Obi da na AA Solomon Okangbuan da kuma na jam’iyyar APM Chichi Ojei duka sun shigar da ƙara gaban kotun ƙorafin zaɓe domin ƙalubalantar nasar Tinubu sa’o’i kafin cikar wa’adin da kundin tsarin mulkin ƙasar ya ba su dama na ƙalubalantar sakamakon zaɓen.

Manyan ‘yan takarar hamayyar biyu Atiku Abubakar da Peter Obi sun nemi kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓen da ta ayyana cewa Tinubu bai ci zaɓen da aka gudanar ba.

Peter Obi ya yi zargin cewa an yi aringizon ƙuri’u a jihohin Rivers da Legas da Taraba da Benue da Adamawa da Imo da Bauchi da Borno da Kaduna da kuma jihar Plateau.

Obi na buƙatar kotun da ta ƙwace takardar shaidar cin zaɓe da hukumar INEC ta ba shi, tare da ba shi sabuwar takardar shaidar cin zaɓe.

Ranar Talata da yamma ne Amurka ta fitar da wata sanarwa tana mai Allah wadai da ƙaruwar razanar da masu kaɗa ƙuri’a da sauran laifukan zaɓe da ta ce an aikata a lokacin zaɓen gwamnoni na ranar 18 ga watan Maris.

daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp