fidelitybank

Jam’iyyun adawa ne suka hana jihar Kano zama lafiya – Abba

Date:

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya zargi wasu mambobin jam’iyyun adawa da haddasa tarzoma da rashin zaman lafiya a jihar.

Gwamnan ya bayyana wannan zargi ne a ranar Laraba yayin taron majalisar zartarwa ta jiha, inda ya ce rikicin baya-bayan nan tsakanin wasu matasa ‘yan daba a tsakiyar birnin Kano ya samo asali ne daga masu ɗaukar nauyin fitintinu.

A cewarsa, rahoton sirri da aka tattauna a taron kwamitin tsaro na jiha a ranar Talata ya bayyana sunayen waɗanda ke da hannu a tashe-tashen hankulan.

Gwamna Yusuf ya ce jam’iyyun adawa ba su farin ciki da zaman lafiya da cigaban da jihar ke rura wutar rigingimun.

Duk da haka, gwamnan ya yi alkawarin ɗaukar matakan gaggawa don kawo ƙarshen dawowar ayyukan ‘yan daba a jihar.

Ya bayyana cewa gwamnatinsa ba za ta yarda wani ya yi ƙoƙarin dagula zaman lafiya a Kano ba.

Ya kuma tabbatar da cewa za su haɗa kai da hukumomin tsaro don magance ayyukan masu tayar da hankali a jihar.

Gwamnan ya sanar da shirye-shiryen sake buɗe cibiyar gyaran hali da ke karamar hukumar Kiru domin sake tarbiyyar matasa da kuma dakile amfani da miyagun ƙwayoyi a jihar.

Haka zalika, Yusuf ya bayyana aniyar gwamnati ta kaddamar da sabuwar majalisar Shura ta malamai 46, wadda ta ƙunshi manyan malamai na addini, masana, da sauran masu ruwa da tsaki, domin ci gaban jihar.

assu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp