fidelitybank

Jam’iyyun adawa ne suka hana jihar Kano zama lafiya – Abba

Date:

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya zargi wasu mambobin jam’iyyun adawa da haddasa tarzoma da rashin zaman lafiya a jihar.

Gwamnan ya bayyana wannan zargi ne a ranar Laraba yayin taron majalisar zartarwa ta jiha, inda ya ce rikicin baya-bayan nan tsakanin wasu matasa ‘yan daba a tsakiyar birnin Kano ya samo asali ne daga masu ɗaukar nauyin fitintinu.

A cewarsa, rahoton sirri da aka tattauna a taron kwamitin tsaro na jiha a ranar Talata ya bayyana sunayen waɗanda ke da hannu a tashe-tashen hankulan.

Gwamna Yusuf ya ce jam’iyyun adawa ba su farin ciki da zaman lafiya da cigaban da jihar ke rura wutar rigingimun.

Duk da haka, gwamnan ya yi alkawarin ɗaukar matakan gaggawa don kawo ƙarshen dawowar ayyukan ‘yan daba a jihar.

Ya bayyana cewa gwamnatinsa ba za ta yarda wani ya yi ƙoƙarin dagula zaman lafiya a Kano ba.

Ya kuma tabbatar da cewa za su haɗa kai da hukumomin tsaro don magance ayyukan masu tayar da hankali a jihar.

Gwamnan ya sanar da shirye-shiryen sake buɗe cibiyar gyaran hali da ke karamar hukumar Kiru domin sake tarbiyyar matasa da kuma dakile amfani da miyagun ƙwayoyi a jihar.

Haka zalika, Yusuf ya bayyana aniyar gwamnati ta kaddamar da sabuwar majalisar Shura ta malamai 46, wadda ta ƙunshi manyan malamai na addini, masana, da sauran masu ruwa da tsaki, domin ci gaban jihar.

leadership newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...
X whatsapp