fidelitybank

Jam’iyyun adawa mu hada hannu don ceto Najeriya daga mulkin jam’iyya guda – Atiku

Date:

Jagoran adawa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubaiar, ya yi kira ga jam’iyyun adawa a ƙasar su haɗa karfi da karfe a wuri ɗaya don tsamo dimokraɗiyyar ƙasar daga tsunduma zuwa mai bin jam’iyya ɗaya.

Ya kuma ja hankali a kan buƙatar yin hattara game da komawar Najeriya, tsarin jam’iyya ɗaya mai mulkin kama-karya.

Wata sanarwa da Paul Ibe, mashawarcin ɗan takarar shugaban ƙasar a zaɓen watan Fabrairun 2023 ya fitar ranar Talata, ta ce Atiku ya yi kiran ne lokacin da ya karɓi bakuncin shugabannin majalisar tuntuɓa tsakanin jam’iyyu ta Najeriya (IPAC).

Tsohon mataimakin shugaban Najeriyar, shi ne ya zo na biyu a zaɓen shugaban ƙasa da aka yi a farkon wannan shekara, wanda Bola Tinubu ya kayar da shi.

A cewarsa, aikin kare mutuncin dimokraɗiyya a ƙasar, ba kawai na mutum ɗaya ba ne.

Ya nunar da cewa hakikanin gaskiya tsarin dimokraɗiyyarmu cikin sauri na komawa zuwa tsarin jam’iyya ɗaya, “kuma tabbas kun sani cewa idan tsarin jam’iyya ɗaya ne da mu, to kawai mu mance da maganar dimokraɗiyya”.

Atiku ya ƙara da cewa “Dukkanmu mun ga yadda jam’iyyar APC ke daɗa mayar da Najeriya zuwa ƙasar mulkin kama-karya mai jam’iyya ɗaya. Idan ba mu zo mun haɗu don kalubalantar abin da jam’iyya mai mulki take ƙoƙarin kafawa ba, dimokraɗiyyarmu za ta sha wahala, kuma sakamakon haka zai shafi hatta zuri’ar da ba a ma haifa ba”.

punch newspaper headlines today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp