fidelitybank

Jam’iyyu hudu sun narke sun koma goyon bayan Atiku

Date:

Kwanaki biyu bayan da jam’iyyar APM ta ruguza tsarinta na goyon bayan jam’iyyar PDP da dan takararta na shugaban kasa a zaben 2023, Alhaji Atiku Abubakar, wasu jam’iyyun siyasa hudu sun bi sahun gaba.

POLITICS NIGERIA ta rawaito cewa, an bayyana hakan ne a hukumance a ranar Asabar a taron yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP a filin wasa na Ribadu da ke Jimeta-Yola a jihar Adamawa.

Jam’iyyun dai su ne Action Peoples Party (APP), Action Alliance (AA), National Rescue Movement (NRM), da kuma African Democratic Congress (ADC).

Da yake magana a madadin sauran shugabannin jam’iyyun siyasa na kasa, shugaban jam’iyyar APM na kasa, Yusuf Mamman Dantalle, ya ce jam’iyyun sun cimma matsayar daukar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP ne saboda shi ne ya fi cancanta a cikin ’yan takara 18.

Sai dai ya ce jam’iyyun za su halarci zabukan gwamnoni, na kasa da na ‘yan majalisun jiha.

Wasu daga cikin jiga-jigan PDP da suka halarci gangamin Adamawa sun hada da gwamnoni Udom Emmanuel (Akwa Ibom), Aminu Tambuwal (Sokoto), Ahmadu Fintiri (Adamawa), Godwin Obaseki (Edo) da kuma Bala Mohammed (Bauchi).

Sauran sun hada da tsohon dan majalisar tarayya, Dino Melaye da Iyorchia Ayu, shugaban jam’iyyar PDP na kasa.

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...
X whatsapp