Kwanaki biyu bayan da jam’iyyar APM ta ruguza tsarinta na goyon bayan jam’iyyar PDP da dan takararta na shugaban kasa a zaben 2023, Alhaji Atiku Abubakar, wasu jam’iyyun siyasa hudu sun bi sahun gaba.
POLITICS NIGERIA ta rawaito cewa, an bayyana hakan ne a hukumance a ranar Asabar a taron yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP a filin wasa na Ribadu da ke Jimeta-Yola a jihar Adamawa.
Jam’iyyun dai su ne Action Peoples Party (APP), Action Alliance (AA), National Rescue Movement (NRM), da kuma African Democratic Congress (ADC).
Da yake magana a madadin sauran shugabannin jam’iyyun siyasa na kasa, shugaban jam’iyyar APM na kasa, Yusuf Mamman Dantalle, ya ce jam’iyyun sun cimma matsayar daukar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP ne saboda shi ne ya fi cancanta a cikin ’yan takara 18.
Sai dai ya ce jam’iyyun za su halarci zabukan gwamnoni, na kasa da na ‘yan majalisun jiha.
Wasu daga cikin jiga-jigan PDP da suka halarci gangamin Adamawa sun hada da gwamnoni Udom Emmanuel (Akwa Ibom), Aminu Tambuwal (Sokoto), Ahmadu Fintiri (Adamawa), Godwin Obaseki (Edo) da kuma Bala Mohammed (Bauchi).
Sauran sun hada da tsohon dan majalisar tarayya, Dino Melaye da Iyorchia Ayu, shugaban jam’iyyar PDP na kasa.