fidelitybank

Jam’iyyu 18 sun yi barazanar kauracewa zaben 2023

Date:

Jam’iyyun siyasa 13 daga cikin jam’iyyu 18 a Najeriya sun yi barazanar kaurace wa babban zaɓen ƙasar da ke tafe matukar Babban Bankin Ƙasar ya ƙara wa’adin amfani da tsoffin kuɗi a ƙasar.

Jam’iyyun sun ce ba za su shiga zaɓen ba matuƙar CBN ya sake tsawaita wa’adin amfani da tsoffin takardun kudin.

Gamayyar ƙungiyar shugabannin jam’iyun, waɗanda suka yaba wa shugaban ƙasar Muhammadu Buhari kan sauya fasalin wasu takardun kuɗin ƙasar, sun dage cewa dole a tabbatar da tsarin.

Shugaban Jam’iyyar Action Alliance A.A Kenneth Udeze, wanda ya yi wa manema labarai jawabi, ya ce ”muna bayyana cewa akalla jam’iyyu 13 daga cikin jam’iyyun ƙasar nan 18 ba za mu shiga zaɓen da ke tafe ba matuƙar aka dakatar ko a aka soke ko aka tsawaita wa’adin fara amfani da sabbin takardun kuɗi”.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatocin jihohin Kaduna da Kogi da Zamfara suka kai ƙarar gwamnatin tarayya gaban Kotun Ƙolin ƙasar, suna neman kotun da ta dakatar da gwamnatin tarayyar daga aiwatar da tsarin wa’adin amfani da tsoffin takardun kuɗi da Babban Bankin ƙasar ya ɓullo da shi.

Matakin da gamayar jam’iyyun suka yi watsi da shi.

A makon da ya gabata ma dai gwamnonin jam’iyyar APC mai mulki suka gana da shugaban ƙasar a fadarsa da ke Villa.

Inda suka buƙace shi da ya sake tsawaita wa’adin amfani da sabbin takardun kudi, sakamakon wahalhalun ƙarancin kudin da jama’ar ƙasar ke fuskanta.

To sai dai a martanin da ya mayar, shugaban ƙasar ya alƙawarta duba tare da magance matsalar cikin kwanaki bakwai.

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp