fidelitybank

Jam’iyyar PRP ta soki Tinubu a kan manufofinsa

Date:

Jam’iyyar PRP ta soki manufofin tattalin arzikin shugaba Bola Tinubu, tana zargin gwamnatinsa da rusa matsakaitan masu abin hannu a Najeriya.

Shugaban PRP, Bello Falalu, ya yi wannan furuci a yayin taron manema labarai da aka gudanar a Abuja a ranar Juma’a, inda ya zargi shugaban kasa da rashin cika alkawarin ingantaccen mulki.

Ya ce babu abin da ya karu sai talautar da al’umma, da kuma tabarbarewar tattalin arzikin kasa.

Ya koka kan manyan sauye-sauyen tattalin arziki, inda ya kaw misalin karancin raguwar tattalin arzikin abun da ake samarwa a cikin ciki (GDP), wanda ya ragu daga Dala biliyan 493 a shekarar 2015 zuwa kimanin Dala biliyan 362 a shekarar 2024.

A cewarsa, wannan raguwar 27% na GDP ya nuna yadda tattalin arzikin Najeriya ke kara tabarbarewa tsawon shekaru tara da suka gabata, abin da ya jefa miliyoyin mutane cikin talauci da koma baya.

Falalu ya kuma soki yadda ake gudanar da kudaden shiga daga cire tallafin man fetur, tsarin canjin kudade da karin farashin wutar lantarki, yana mai cewa ba su samar da kayan more rayuwa da aka yi alkawari ba.

Ya kara da cewa harajin 38% da bankuna ke caji yana hana bunkasar kananan da matsakaitan masana’antu (SMEs), wanda shi ne jigon ci gaban tattalin arziki.

Falalu ya bayyana shirin tattaunawa tsakanin PRP da ADC kan yiwuwar kafa kawance ko hadewa, yana mai jaddada bukatar samun zabe na gaskiya don samun kyakkyawar makoma ga matasa.

Ya fadi fatansa na cewa sauran jam’iyyu su hada hannu wajen hadewa waje guda kafin zabe mai zuwa.

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp