fidelitybank

Jam’iyyar PRP ta soki Tinubu a kan manufofinsa

Date:

Jam’iyyar PRP ta soki manufofin tattalin arzikin shugaba Bola Tinubu, tana zargin gwamnatinsa da rusa matsakaitan masu abin hannu a Najeriya.

Shugaban PRP, Bello Falalu, ya yi wannan furuci a yayin taron manema labarai da aka gudanar a Abuja a ranar Juma’a, inda ya zargi shugaban kasa da rashin cika alkawarin ingantaccen mulki.

Ya ce babu abin da ya karu sai talautar da al’umma, da kuma tabarbarewar tattalin arzikin kasa.

Ya koka kan manyan sauye-sauyen tattalin arziki, inda ya kaw misalin karancin raguwar tattalin arzikin abun da ake samarwa a cikin ciki (GDP), wanda ya ragu daga Dala biliyan 493 a shekarar 2015 zuwa kimanin Dala biliyan 362 a shekarar 2024.

A cewarsa, wannan raguwar 27% na GDP ya nuna yadda tattalin arzikin Najeriya ke kara tabarbarewa tsawon shekaru tara da suka gabata, abin da ya jefa miliyoyin mutane cikin talauci da koma baya.

Falalu ya kuma soki yadda ake gudanar da kudaden shiga daga cire tallafin man fetur, tsarin canjin kudade da karin farashin wutar lantarki, yana mai cewa ba su samar da kayan more rayuwa da aka yi alkawari ba.

Ya kara da cewa harajin 38% da bankuna ke caji yana hana bunkasar kananan da matsakaitan masana’antu (SMEs), wanda shi ne jigon ci gaban tattalin arziki.

Falalu ya bayyana shirin tattaunawa tsakanin PRP da ADC kan yiwuwar kafa kawance ko hadewa, yana mai jaddada bukatar samun zabe na gaskiya don samun kyakkyawar makoma ga matasa.

Ya fadi fatansa na cewa sauran jam’iyyu su hada hannu wajen hadewa waje guda kafin zabe mai zuwa.

daily post newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp