Jam’iyyar adawa ta LP ta naɗa tsohuwar ministar kuɗi, Sanata Nenadi Usman, a matsayin sabuwar shugabar riƙon ƙwarya ta jam’iyyar.
Haka kuma jam’iyyar ta sanar da naɗin tsohon mataimakin shugaban marasa rinjayen na majalisar dattawa ƙasar, Sanata Darlington Nwokocha a matsayin sakataren riƙo na jam’iyyar.
Jam’iyyar ta kuma ɗora wa – kwamitin riƙon ƙwaryar mai mambobi 29 – alhakin gudanar da zaɓukan shugabannin jam’iyyar a matakai daban-daban cikin kwanaki 90 masu zuwa.
Masu ruwa da tsaki na jam’iyyar ne dai ciki har da jagoran jam’iyyar kuma ɗan takararta na shugaban ƙasa Peter Obi da mataimakinsa suka gudanar da taron naɗa kwamitin riƙo na jam’iyyar a gidan gwamnatin jihar Abia, kamar yadda sakataren yaɗa labaran gwamnan jihar ya bayyana cikin wata sanarwa da ya fitar.
To sai dai ɓangaren shugaban jam’iyyar, Julius Abure ya yi watsi da zaman masu ruwa da tsaki na jam’iyyar suka jagoranta, tare da naɗin Sanata Nenadi Usman, suna masu bayyana shi da wanda ya saɓa wa ƙa’ida.