fidelitybank

Jam’iyyar LP ta nada tsohuwar ministar kudi a matsayin shugaba

Date:

Jam’iyyar adawa ta LP ta naɗa tsohuwar ministar kuɗi, Sanata Nenadi Usman, a matsayin sabuwar shugabar riƙon ƙwarya ta jam’iyyar.

Haka kuma jam’iyyar ta sanar da naɗin tsohon mataimakin shugaban marasa rinjayen na majalisar dattawa ƙasar, Sanata Darlington Nwokocha a matsayin sakataren riƙo na jam’iyyar.

Jam’iyyar ta kuma ɗora wa – kwamitin riƙon ƙwaryar mai mambobi 29 – alhakin gudanar da zaɓukan shugabannin jam’iyyar a matakai daban-daban cikin kwanaki 90 masu zuwa.

Masu ruwa da tsaki na jam’iyyar ne dai ciki har da jagoran jam’iyyar kuma ɗan takararta na shugaban ƙasa Peter Obi da mataimakinsa suka gudanar da taron naɗa kwamitin riƙo na jam’iyyar a gidan gwamnatin jihar Abia, kamar yadda sakataren yaɗa labaran gwamnan jihar ya bayyana cikin wata sanarwa da ya fitar.

To sai dai ɓangaren shugaban jam’iyyar, Julius Abure ya yi watsi da zaman masu ruwa da tsaki na jam’iyyar suka jagoranta, tare da naɗin Sanata Nenadi Usman, suna masu bayyana shi da wanda ya saɓa wa ƙa’ida.

dailypost news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp