fidelitybank

Jam’iyyar LP da ta ke mulki a jihar Abia ta sha ka yi a dukkannin zaɓen ƙananan hukumomi 17

Date:

Jam’iyyar Labour da ke mulkin jihar Abia ta kasa cin ko da ɗaya daga ƙananan hukumomin jihar 17 a zaɓen ƙananan hukumomin da aka yi a jiya Asabar.

A maimakon haka jam’iyyar Zenith Labour Party (ZLP), ce ta cinye yawancin ƙananan hukumomin inda ta samu 15 daga cikin 17.

Jam’iyyar Young Progressives Party (YPP) ce ta ci ragowar ƙananan hukumomin biyu – ƙaramar hukumar Ugwunagbo da kuma Osisioma Ngwa.

Shugaban hukumar zaɓen jihar, (ABSIEC), George Chima, shi ne ya bayyana sakamakon a ofishin hukumar da ke babban birnin jihar, Umuahia, a jiya Asabar.

Mista Chima, ya bayyana gamsuwarsa da yadda zaɓen da ya ce sama da jam’iyyu 12 suka shiga, ya gudana.

Sakamakon rigimar da ake yi ta shugabancin jam’iyyar Labour a tarayya, ‘yantakarar da ake gani suna da goyon bayan gwamnan jihar Alex Otti, sun tsaya takara ne a jam’iyyar Zenith Labour Party, wadda ta ci kujeru 15 ɗin.

Shugabancin jam’iyyar Labour na ƙasa na fama da rikici inda ake da ɓangare biyu, na tsohuwar ministar kuɗi Sanata Nenadi Usman, da Gwamna Otti ke bi, da kuma ɓangaren Julius Abure.

sahara hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp