fidelitybank

Jam’iyyar Labour na shirin gudanar da gagarumar zanga-zanga a Abuja

Date:

Jam’iyyar Labour ta yi barazanar gudanar da zanga-zanga a ofisoshin hukumar zaɓe da ke faɗin ƙasar kan ƙin ba ta damar duba na’urorin BVAS da aka gudanar da zaɓen shugaban ƙasar da su ranar 25 ga watan Fabrairu.

Dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Peter Obi ya nemi kotu da ta hana INEC sake saita na’ororin BVAS da aka yi amfani da su a zaɓen shugaban ƙasar.

To amma kotun ta bai wa INEC damar saita na’urorin tare da bai wa Obi damar duba kayayyakin da aka gudanar da zaɓen shugaban ƙasar da su.

Karanta Wannan: A na yunkurin kashe ni a Legas – Dan takarar LP

To sai dai kwanaki bayan hukuncin kotun mai magana da yawun kwamityin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyyar Dr Yunusa Tanko ya zargi hukumar zaɓen da ƙin bin umarnin kotu.

“Yayin da muke magana a yanzu INEC ta zaɓi bin umarnin da kotu ta ba ta na sake saita na’urorin BVAS, aikin da take cikin yi yanzu haka, sannan kuma ta ƙi bin umarnin damar da kotun ta ba mu na duba kayyakin da aka gudanar da aikin zaɓen,” kamar yadda ya bayyana a sanarwar da ya fitar.

“Dan haka za mu kira magoya bayanmu da su gudanar da zanga-zangar lumana wadda doka ta amince da ita, a ofisoshin hukumar zaɓe da ke faɗin ƙasar nan”.

Ya ƙara da cewa abin da ya sa ba za su gudanar da zanga-zangar a kan titunan ƙasar ba, shi ne ba sa so a ɗauki zanga-zangar tasu a matsayin tayar da hankali.

newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...

An binne marigayi Muhammadu Buhari a gidansa na Daura

An binne gawar tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a...

Pillars ta dauki yan wasa guda biyu

Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta tabbatar da...

An cafke ‘yan Daba 28 a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ta samu...

Na yafe wa Buhari duk abun da ya yi min – Buba Galadima

Buba Galadima, wanda tsohon abokin marigayi Muhammadu Buhari ne...

Shugabannin Afrika za su halarci jana’izar Buhari

Ana sa ran wasu daga cikin shugabannin ƙasashen Afirka...

Yadda ake shirye-shiryen jana’izar Buhari a Daura

A yanzu haka dai alumma na ta tururuwa domin...
X whatsapp