Jam’iyyar APC mai mulki tana da mafi girman karfin iya yiwa Najeriya aiki mai kyau da kuma tabbatar da ci gabanta, a cewar mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo, SAN.
Farfesa Osinbajo ya bayyana haka ne ranar Alhamis a jihar Ribas, a ci gaba da tuntubar da yake yi a fadin kasa tare da masu ruwa da tsaki da kuma wakilan jam’iyyar All Progressives Congress (APC).
Da yake jawabi a takaice da manema labarai bayan ganawarsa da wakilan jihar, mataimakin shugaban kasar ya tabbatar da daukaka da ci gaban Najeriya a nan gaba, inda ya ce “mu ma, ba shakka, muna gaba daya kan ra’ayin cewa, jam’iyyar na bukatar hadin kai. Don haka duk abin da ya kamata a yi ana yin shi ne, kuma za a yi shi ne domin tabbatar da hadin kan ‘yan takara”.
Ya ci gaba da cewa, “Ba shakka jam’iyyar mu ce, kamar yadda kuka sani, ba jam’iyya mai mulki kadai ba ce, jam’iyyar da ke da babban abin da za ta iya yi wa kasar nan.