Jam’iyyar APC mai mulki a jihar Kano, ta wayi gari cikin dakon wani sabon tsarin da uwar jam’iyyar ta kira “wanda zai shigar da kowa a dama da shi” cikin harkar shugabanci.
Duka ɓangarorin biyu, tsagin Sanata Shekarau ko kuma G7, da kuma na Gwamna Ganduje na kira ga uwar jam’iyyar ta tabbatar da adalci.
Jam’iyyar APC ta ce, bayan sanar da wannan tsari, za ta kafa wani babban kwamiti da zai je Kano, domin tabbatar da cikakken aiki da shi.
Tun a shekarar 2021 ne, bangaren Gwamna Ganduje da na Sanata Shekarau, suka shata layi a tsakanin juna.