fidelitybank

Jam’iyyar ADC alheri ce ga siyasar Najeriya – Femi Gbajabiamila

Date:

Shugaban ma’aikata na fadar gwamnatin Najeriya, Femi Gbajabiamila ya ce haɗakar ƴansiyasa a jam’iyyar ADC alheri ce ga siyasar Najeriya, wanda a cewarsa hakan zai taimaka waje hana ƙasar faɗawa cikin siyasar jam’iyyar ƙwaya ɗaya tal.

Gbajabiamila ya bayyana haka ne jim kaɗan ya kaɗa ƙuri’arsa a zaɓen ƙananan hukumomin da aka yi a jihar Legas a jiya Asabar a mazaɓarsa da ke Surulere, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Sai dai tsohon shugaban majalisar wakilan ƙasar ya bayyana shakkunsa kan haɗakar, inda ya ce ce ba ya tunanin za ta yi wani tasirin a-zo-a-gani.

“Muna maraba da samar da haɗakar. Ai ba wannan ba ne karo na farko da aka samu haɗakar ƴansiyasar a wannan ƙasar tamu,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa “a dimokuraɗiyya ana buƙatar hamayya mai ƙarfi, domin idan babu hamayya mai ƙarfi, za mu iya faɗawa siyasar jam’iyyar ɗaya,” in ji shi.

A Najeriya dai fitatun ƴan jam’iyyun hamayya irin su Atiku Abubakar da Peter Obi da Nasir El-Rufai da Rotimi Amaechi da sauransu ne suka haɗu a jam’iyyar ADC domin fuskantar zaɓen 2027, inda suke fata za su kayar da Bola Tinubu.

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Najeriya na cece-kuce dangane da rasuwar Muhammadu Buhari

Mutuwar shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta bar cece-kuce ga...

Da Ɗumi-Ɗumi: Kashim Shettima zai rako gawar Muhammadu Buhari zuwa Najeriya

Tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya rasu. Ya rasu ne...

Ina Tinubu ya ke ya ɓata ba bayani – ADC

Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC, ta soki Shugaba,...

Koriya ta Arewa za ta ba Rasha ƙarin sojoji domin yaƙin Ukraine

Shugaban Koriya ta Arewa Kim Jong Un ya yi...

Jam’iyyar ADC alheri ce ga siyasar Najeriya – Femi Gbajabiamila

Shugaban ma'aikata na fadar gwamnatin Najeriya, Femi Gbajabiamila ya...

Tinubu na yunkurin tauye hakkin ma’aikata – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban ƙasa a Najeriya, Atiku Abubakar, ya...

Trump ya lafta wa ƙasashen Tarayyar Turai da Mexico harajin kashi 30

Shugaban Amurka Donald Trump ya lafta wa ƙasashen ƙungiyar...

INEC ta ce za ta buɗe shafin intanet domin rajistar sababbin jam’iyyu

Huhukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC, ta ce nan...

EFCC na neman Rabi’u Auwalu Tijjani ruwa a jallo a Kano

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin...

An gano musabbabin hatsarin jirgin saman Indiya

Masu bincike sun bayyana sakamako na farko-farko game da...

Amurka ta haramta wa shugaban kasar Cuba shiga kasar

Amurka a karon farko ta ƙaƙaba takunkumi kan shugaban...

An kashe mutum 6,800 tare da sace 5,402 a 2025 Najeriya – Rahoto

Alƙaluma na nuna cewa an kashe mutum dubu shida...
X whatsapp