Gwamnonin Douye Diri da Nyesom Wike na Bayelsa da Rivers sun ce, jam’iyyar PDP ce Za ta iya ceto Najeriya ta hanyar samar da shugaban kasa.
Gwamnonin biyu sun yi magana ne a lokacin da Wike ya jagoranci wata tawaga mai karfi daga jihar Ribas, domin kai ziyarar ban girma ga Diri a gidan gwamnati na Yenagoa.
A baya-bayan nan ne dai Wike ke kallon guguwar a lokacin da kungiyar Ijaw National Congress (INC) da kungiyar matasan Ijaw (IYC) su ka yi masa kaca-kaca a kan abin da su ka dauka na kin jinin kabilar Ijaw da ya yi a lokacin bikin ranar Ogoni.
Majiyarmu ta bayyana cewa tattaunawar da gwamnonin biyu su ka yi ta ta’allaka ne kan karfafa dankon hadin kai tsakanin jihohin biyu da jam’iyyar PDP.
Ya bayyana fadar shugaban kasa a matsayin ofishi mai tsarki, inda ya ce, an mayar da jam’iyyar PDP ne domin ganin ta lashe zaben shugaban kasa a zaben 2023 mai zuwa.