Kungiyar malaman jami’o’i ta kasa (ASUU) ta musanta karbar tsabar kudi Naira biliyan 52 daga wajen gwamnatin tarayya.
Shugaban kungiyar ta ASUU shiyar Kano, Farfesa Abdulkadir Muhammad ya bayyana hakan a ganawar sa da manema labarai, ya ce, kungiyar ta karbi Naira biliyan 22 daga gwamnatin tarayya, su ka yi amfani da kaso 75 cikin kudin, yayin da su ka raba kaso 25 ga sauran kungiyoyi da ke karkashin kungiyar.
Ya kara da cewa”Labarin da a ke yadawa cewa sun karbi Naira biliyan 52 karya ne, gwamnati ce ta fito da shi, domin batawa kungiyar mu suna, saboda kungiyar ta dage a kan sai an kawo gyara a harkar ilimi”.
Farfesa Abdulkadir Muhammad ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta yi kokari wajen kawo karshen matsalar tsaro dake addabar kasar nan.
Ministan kwadago, Chris Ngige ne dai ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta fitar da kudaden domin biyan malaman jami’an bashin alawus da albashi na fiye da watanni 20 da su ke bin gwamnatin.