fidelitybank

Jami’in mu bai saci naira biliyan 6.5 ba – Gwamnatin Kano

Date:

Gwamnatin Jihar Kano ta karyata rahoton da ya zargi daraktan tsare-tsare na fadar Gwamnati, Abdullahi Ibrahim Rogo, da karkatar da sama da naira biliyan 6.5 daga baitul-mali.

A wata sanarwa, da Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar ta ce, gwamnatin ta ce, duk kudaden dake fita daga asusun ta ana gudanar da su ne bisa kasafin kudi, ba tare da wani jami’i ya mallaki ikon kashe kuɗi yadda ya ga dama ba.

Sanarwar ta bayyana cewa zargin da aka wallafa a Daily Nigerian ya samo asali ne daga adawa da ke ƙoƙarin bata sunan gwamnati kafin 2027, tare da jaddada cewa Rogo mutum ne mai gaskiya da amana.

Gwamnatin ta kuma tunatar da yadda tsohuwar gwamnatin Abdullahi Ganduje ta kashe fiye da naira biliyan 20 cikin watanni uku kacal a shekarar 2023, tana mai cewa mutanen Kano sun san irin cin hanci da rashawa da taƙaita dukiya da aka yi a baya.

Wannan zargi ƙarya ce ta siyasa. Gwamnatin Abba Kabir Yusuf ba za ta bar ƙoƙarin bata sunan jami’anta ya yi tasiri ba,” in ji sanarwar.

Gwamnati ta ce za ta ci gaba da gudanar da mulki cikin gaskiya da rikon amana, tare da gargadin masu yada ƙarya da siyasar bata suna.

punch news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp