fidelitybank

Jami’ar BUK ta daga likafar Sheikh Sani Umar Rijiyar Lemo zuwa Farfesa

Date:

Jami’ar Bayero da ke Kano ta sanar da daga matsayin Sheikh Sani Umar Rijiyar Lemo zuwa Farfesa a fannin Hadith.

Wannan na kunshe a wata sanarwa da jami’ar ta fitar a yammacin ranar Juma’a.

Shafin Facebook na Sheikh Sani Umar Rijiyar Lemo ya tabbatar da wannan cigaba, inda mabiyansa suka yi ta taya shi murna bisa wannan babban matsayi da ya samu.

Sheikh Sani Umar Rijiyar Lemo, wanda yanzu ya zama Farfesa, yana daga cikin fitattun malamai masu tasiri a harkar addinin Musulunci a Najeriya. Malamin ya shahara wajen koyar da tafsirin Al-Qur’ani mai girma da wa’azantarwa ga al’umma a ciki da wajen Najeriya.

A matsayinsa na malami a jami’ar Bayero, Farfesa Sani Umar Rijiyar Lemo yana koyarwa a sashen addinin Musulunci, inda yake ilmantar da dalibai tare da bayar da gudunmawa ga cigaban al’umma. Wannan sabon matsayi zai kara masa damar cigaba da taka rawa a fannin koyarwa.

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp